Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 22:22-39 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Da suka ji haka, sai suka yi mamaki, suka rabu da shi, suka yi tafiyarsu.

23. A ran nan sai waɗansu Sadukiyawa (su da suke cewa, ba tashin matattu) suka zo wurinsa, suka yi masa tambaya,

24. suka ce, “Malam, Musa dai ya ce, ‘In mutum ya mutu, bai bar na baya ba, sai lalle ɗan'uwansa ya auri matar, ya haifa wa ɗan'uwansa 'ya'ya.’

25. To, an yi waɗansu 'yan'uwa maza bakwai a cikinmu. Na farkon ya yi aure, da ya rasu, da yake bai haifu kuma ba, sai ya bar wa ɗan'uwansa matarsa.

26. Haka ya faru ga na biyun da na ukun, har ya kai kan na bakwai ɗin.

27. Bayansu duka sai matar ta rasu.

28. To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu, su bakwai ɗin? Don duk sun aure ta.”

29. Amma Yesu ya amsa musu ya ce, “Kun ɓăta ne, domin ba ku san Littattafai ba, ba ku kuma san ikon Allah ba.

30. Domin a tashin matattu, ba a aure, ba a aurarwa, sai dai kamar mala'ikun da suke Sama ake.

31. Game da tashin matattu, ashe, ba ku taɓa karanta abin da Allah ya ce muku ba? cewa,

32. ‘Ni ne Allahn Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.’ Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba.”

33. Da jama'a suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.

34. Amma da Farisiyawa suka ji ya ƙure Sadukiyawa, suka taru.

35. Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Attaura, ya yi masa tambaya, yana gwada shi, ya ce,

36. “Malam, wane umarni ne mafi girma a cikin Attaura?”

37. Ya ce masa, “Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.

38. Wannan shi ne babban umarni na farko.

39. Na biyu kuma kamarsa yake, ‘Ka ƙaunaci ɗan'uwanka kamar kanka.’

Karanta cikakken babi Mat 22