Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 17:13-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Sa'an nan ne almajiran suka gane, ashe, zancen Yahaya Maibaftisma yake yi musu.

14. Da suka isa wurin taro, sai wani mutum ya zo gare shi, ya durƙusa a gabansa, ya ce,

15. “Ya Ubangiji, ka ji tausayin ɗana, yana farfaɗiya, yana shan wuya ƙwarai, sau da yawa yakan faɗa wuta da kuma ruwa.

16. Na kuwa kai shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”

Karanta cikakken babi Mat 17