Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 9:27-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Amma Yesu ya kama hannunsa ya tashe shi, ya kuwa tashi tsaye.

28. Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a keɓe suka ce, “Me ya sa mu muka kasa fitar da shi?”

29. Sai ya ce musu, “Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a.”

30. Sai suka tashi daga nan, suka ratsa ƙasar Galili, bai kuwa so kowa ya sani ba,

31. domin yana koya wa almajiransa ne, yana ce musu, “Za a ba da Ɗan Mutum ga mutane, za su kuwa kashe shi, sa'ad da aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi.”

32. Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambaya tasa.

33. Suka zo Kafarnahum. Da ya shiga gida sai ya tambaye su, “Muhawarar me kuka yi a hanya?”

34. Amma suka yi shiru, don a hanya sun yi muhawarar ko wane ne babbansu.

35. Sai ya zauna, ya kira sha biyun nan, ya ce musu, “Kowa yake son yă zama shugaba, lalle ne yă zama na ƙarshe duka, baran kowa kuma.”

36. Sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa shi a tsakiyarsu, ya rungume shi, ya ce musu,

Karanta cikakken babi Mar 9