Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 5:10-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Sai ya roƙi Yesu da gaske kada ya kore su daga ƙasar.

11. To, wurin nan kuwa da wani babban garken alade na kiwo a gangaren dutsen.

12. Aljannun nan suka roƙe shi suke ce, “Tura mu wajen aladun nan, mu shiga su.”

13. Ya kuwa yardar musu. Sai baƙaƙen aljannun suka fita, suka shiga aladun. Garken kuwa wajen alade dubu biyu, suka rugungunto ta gangaren, suka fāɗa tekun, suka halaka a ruwa.

14. Daga nan sai 'yan kiwon aladen suka gudu, suka ba da labari birni da ƙauye. Jama'a suka zo su ga abin da ya auku.

15. Da suka zo wurin Yesu suka ga mai aljannun nan a zaune, saye da tufa, cikin hankalinsa kuma, wato mai aljannun nan masu yawa a dā, sai suka tsorata.

16. Waɗanda aka yi abin a kan idonsu kuwa, suka farfaɗi abin da ya gudana ga mai aljannun da kuma aladen.

17. Sai suka fara roƙon Yesu ya bar musu ƙasarsu.

18. Yana shiga jirgi ke nan, sai mai aljannun nan a dā ya roƙe shi izinin zama a gunsa.

19. Amma Yesu bai yardar masa ba, ya ce masa, “Tafi gida wurin 'yan'uwanka, ka faɗa musu irin manyan abubuwan da Ubangiji ya yi maka, da kuma yadda ya ji tausayinka.”

20. Sai ya tafi, ya shiga baza labari a Dikafolis na irin manyan abubuwan da Yesu ya yi masa. Duk mutane kuwa suka yi al'ajabi.

21. Da Yesu ya sāke haye ƙetare cikin jirgi, sai babban taro ya kewaye shi. Shi kuwa yana bakin tekun.

22. Sai ga wani daga cikin shugabannin majami'a, mai suna Yayirus. Da ganin Yesu kuwa ya fāɗi a gabansa,

Karanta cikakken babi Mar 5