Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 4:8-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Waɗansu kuma suka faɗa a ƙasa mai kyau, suka yi yabanya, suka girma, suka yi tsaba, waɗansu riɓi talatin talatin, waɗansu sittin sittin, waɗansu ma har ɗari ɗari.”

9. Sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

10. Da suka kaɗaita, masu binsa da su sha biyun nan suka tambaye shi ma'anar misalan.

11. Sai ya ce musu, “Ku kam, an yardar muku ku san asirin Mulkin Allah, amma ga waɗanda ba sa cikinku, kome sai a cikin misali,

12. don gani da ido kam, su gani, amma ba da zuci ba. Ji kuma, su ji, amma ba za su fahimta ba, wai don kada su juyo a yafe musu.”

13. Ya ce musu, “Ashe, ba ku fahimci wannan misali ba? Ƙaƙa za ku fahimci sauran ke nan?

Karanta cikakken babi Mar 4