Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 4:29-40 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Sa'ad da amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi ke nan.”

30. Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta Mulkin Allah? Ko kuwa da wane misali za mu misalta shi?

31. Kamar ƙwayar mastad da yake, wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi ƙanƙantar ƙwayoyi a duniya,

32. duk da haka in an shuka ta, sai ta girma ta fi duk sauran ganye, ta yi manyan rassa, har tsuntsaye su iya sauka a inuwarta.”

33. Da misalai da yawa irin waɗannan Yesu ya yi musu Maganar Allah, daidai gwargwadon ganewa tasu.

34. Ba ya faɗa musu kome sai da misali, amma a keɓe yakan bayyana wa almajiransa kome.

35. A ran nan da maraice ya ce musu, “mu haye can ƙetare.”

36. Da suka bar taron, suka tafi da shi yadda yake a cikin jirgin, waɗansu jirage kuma na tare da shi.

37. Sai babban hadari mai iska ya taso, raƙuman ruwa kuma na ta fantsama cikin jirgin, har jirgin ya tasar wa cika da ruwa.

38. Yesu kuwa na daga ƙarshen baya na jirgin a kan matashi, yana barci. Sai suka tashe shi, suka ce masa, “Malam, za mu hallaka ba ka kula ba ko?”

39. Sai ya farka, ya tsawata wa iskar, ya kuma ce wa ruwan tekun, “Natsu! Ka yi shiru!” Sai iskar ta kwanta, wurin duk ya yi tsit.

40. Ya ce musu, “Don me kuka firgita haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”

Karanta cikakken babi Mar 4