Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 4:23-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. In da mai kunnen ji, yă ji.”

24. Sai ya ce musu, “Ku ji. Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.

25. Domin mai abu akan ƙara wa. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.”

26. Ya ce kuma, “Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a ƙasa.

27. A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma, bai kuwa san ta yadda aka yi ba.

28. Ƙasa da kanta takan ba da amfani, tsiro shi ne na farko, sa'an nan kai, sai kuma ƙwaƙƙwarar ƙwaya a kan.

29. Sa'ad da amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi ke nan.”

30. Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta Mulkin Allah? Ko kuwa da wane misali za mu misalta shi?

31. Kamar ƙwayar mastad da yake, wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi ƙanƙantar ƙwayoyi a duniya,

32. duk da haka in an shuka ta, sai ta girma ta fi duk sauran ganye, ta yi manyan rassa, har tsuntsaye su iya sauka a inuwarta.”

33. Da misalai da yawa irin waɗannan Yesu ya yi musu Maganar Allah, daidai gwargwadon ganewa tasu.

34. Ba ya faɗa musu kome sai da misali, amma a keɓe yakan bayyana wa almajiransa kome.

35. A ran nan da maraice ya ce musu, “mu haye can ƙetare.”

36. Da suka bar taron, suka tafi da shi yadda yake a cikin jirgin, waɗansu jirage kuma na tare da shi.

Karanta cikakken babi Mar 4