Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 4:13-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Ya ce musu, “Ashe, ba ku fahimci wannan misali ba? Ƙaƙa za ku fahimci sauran ke nan?

14. Mai shukan nan fa Maganar Allah yake shukawa.

15. Waɗanda suka fāda a hanya kuwa, su ne kwatancin waɗanda aka shuka Maganar a zuciya tasu. Da zarar sun ji, nan da nan sai Shaiɗan ya zo ya ɗauke Maganar da aka shuka a zuciya tasu.

16. Haka kuma waɗanda aka shuka a wuri mai duwatsu, su ne waɗanda da zarar sun ji Maganar sai su karɓa da farin ciki.

Karanta cikakken babi Mar 4