Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 15:32-39 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Almasihun nan, Sarkin Isra'ila, yă sauko mana daga gicciyen yanzu, mu kuwa mu gani mu ba da gaskiya.” Waɗanda aka gicciye tare da shi su ma suka zazzage shi.

33. Daidai rana tsaka, sai duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma.

34. Da ƙarfe ukun sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktāna?” wato “Ya Allahna, Ya Allahna, don me ka yashe ni?”

35. Da waɗansu na tsaitsayen suka ji haka, suka ce, “Kun ji yana kiran Iliya.”

36. Sai ɗayansu ya yiwo gudu, ya jiƙo wani soso da ruwan tsami, ya soka a sanda, ya miƙa masa yă sha, yana cewa, “Bari mu gani ko Iliya zai zo ya sauko da shi.”

37. Sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi, kana ya cika.

38. Sa'an nan labulen da yake cikin Haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa.

39. Sa'ad da jarumi ɗin da yake tsaye yana kallon Yesu, ya ga yadda ya mutu haka, sai ya ce, “Hakika mutumin nan Ɗan Allah ne!”

Karanta cikakken babi Mar 15