Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 14:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Shi kuwa zai nuna muku wani babban soron bene mai kaya a shirye. A nan za ku shirya mana.”

16. Sai almajiran suka tashi, suka shiga gari, suka kuwa tarar kamar yadda ya faɗa musu, suka shirya Idin Ƙetarewa.

17. Da magariba ta yi, sai ya zo tare da sha biyun nan.

18. Suna cin abinci ke nan, sai Yesu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ɗayanku zai bashe ni, wanda muke ci tare.”

19. Suka fara baƙin ciki, suna ce masa da ɗaya ɗaya, “Ni ne?”

20. Sai ya ce musu, “Ɗaya daga cikin sha biyun nan ne dai, wanda muke ci ƙwarya ɗaya.

Karanta cikakken babi Mar 14