Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 14:12-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. A ranar farko ta idin abinci marar yisti, wato ran da aka saba yanka ɗan ragon Idin Ƙetarewa, sai almajiransa suka ce masa, “Ina kake so mu je mu shirya maka cin Idin Ƙetarewa?”

13. Sai ya aiki almajiransa biyu, ya ce musu, “Ku shiga gari, can za ku gamu da wani mutum ɗauke da tulun ruwa, ku bi shi.

14. Duk gidan da ya shiga, ku ce wa maigidan, ‘In ji Malam, ina masaukin da zai ci Idin Ƙetarewa da almajiransa?’

15. Shi kuwa zai nuna muku wani babban soron bene mai kaya a shirye. A nan za ku shirya mana.”

16. Sai almajiran suka tashi, suka shiga gari, suka kuwa tarar kamar yadda ya faɗa musu, suka shirya Idin Ƙetarewa.

17. Da magariba ta yi, sai ya zo tare da sha biyun nan.

Karanta cikakken babi Mar 14