Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 14:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sauran kwana biyu a yi Idin Ƙetarewa da idin abinci marar yisti, sai manyan firistoci da malaman Attaura suka nemi hanyar kama Yesu da makirci, su kashe shi,

2. don sun ce, “Ba dai a lokacin idi ba, don kaɗa jama'a su yi hargitsi.”

3. Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana cin abinci ke nan, sai ga wata mace ta zo da wani ɗan tulu na man ƙanshi na nardi tsantsa, mai tsadar gaske. Sai ta fasa ulun, ta tsiyaye masa man a kā.

4. Waɗansu kuwa da suka ji haushi, suka ce wa juna, “Mene ne na ɓata mai haka?

Karanta cikakken babi Mar 14