Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 12:7-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Amma manoman nan suka ce wa juna, ‘Ai, wannan shi ne magajin. Ku zo mu kashe shi, gādon yă zama namu.’

8. Sai suka kama shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge.

9. To, me ubangijin garkan nan zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar.

10. Ashe, ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba? cewa,‘Dutsen da magina suka ƙi,Shi ne ya zama mafificin dutsen gini.

11. Wannan aikin Ubangiji ne,A gare mu kuwa abin al'ajabi ne.’ ”

12. Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi misalin, amma suna jin tsoron jama'a. Don haka suka ƙyale shi, suka tafi.

13. Suka aiko masa da waɗansu Farisiyawa da mutanen Hirudus, don su burma shi cikin magana tasa.

14. Da suka zo, suka ce masa, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, ba ka kuma zaɓen kowa, domin ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?

15. Mu biya, ko kada mu biya?” Shi kuwa da ya gane makircinsu, ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku kawo mini dinari in gani.”

16. Suka kawo masa. Ya ce musu, “Suran nan da sunan nan na wane ne?” Suka ce masa, “Na Kaisar ne.”

Karanta cikakken babi Mar 12