Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 1:26-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Sai baƙin aljanin ya buge shi, jikinsa na rawa, ya yi ihu, ya rabu da shi.

27. Duk suka yi mamaki, har suka tanttambayi juna suna cewa, “Kai, mene ne haka? Tabɗi! Yau ga baƙuwar koyarwa! Har baƙaƙen aljannu ma yake yi wa umarni gabagaɗi, suna kuwa yi masa biyayya!”

28. Nan da nan sai ya shahara a ko'ina duk kewayen ƙasar Galili.

29. Da fitarsu daga majami'a, sai suka shiga gidan su Bitrus da Andarawas, tare da Yakubu da Yahaya.

30. Surukar Bitrus kuwa na kwance tana zazzaɓi, nan da nan suka ba shi labarinta.

31. Sai ya matso, ya kama hannunta, ya tashe ta, zazzaɓin kuwa ya sake ta, har ta yi musu hidima.

32. Da magariba, bayan faɗuwar rana, aka kakkawo masa dukan marasa lafiya, da masu aljannu.

33. Sai duk garin ya haɗu a ƙofar gidan.

34. Ya warkar da marasa lafiya da yawa, masu cuta iri iri, ya kuma fitar wa mutane aljannu da yawa. Bai ko yarda aljannun su yi wata magana ba, domin sun san shi.

35. Da asussuba ya tashi ya fita, ya tafi wani wuri inda ba kowa, ya yi addu'a a can.

Karanta cikakken babi Mar 1