Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 1:18-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Nan da nan kuwa suka watsar da tarunansu, suka bi shi.

19. Da ya ci gaba kaɗan, sai ya ga Yakubu ɗan Zabadi, da ɗan'uwansa Yahaya, suna cikin jirginsu suna gyaran taruna.

20. Nan da nan da ya kira su, suka bar ubansu Zabadi a cikin jirgin tare da ma'aikata, suka bi shi.

21. Suka shiga Kafarnahum. Ran Asabar kuwa, ya shiga majami'a yana koyarwa.

22. Sun yi mamakin koyarwa tasa, domin yana koya musu da hakikan cewa, ba kamar malaman Attaura ba.

23. Nan take sai ga wani mutum mai baƙin aljan a majami'arsu, yana ihu,

24. yana cewa, “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne ka hallaka mu? Na san ko wane ne kai, Mai Tsarkin nan ne kai na Allah.”

25. Yesu ya kwaɓe shi ya ce, “Yi shiru! Rabu da shi!”

26. Sai baƙin aljanin ya buge shi, jikinsa na rawa, ya yi ihu, ya rabu da shi.

27. Duk suka yi mamaki, har suka tanttambayi juna suna cewa, “Kai, mene ne haka? Tabɗi! Yau ga baƙuwar koyarwa! Har baƙaƙen aljannu ma yake yi wa umarni gabagaɗi, suna kuwa yi masa biyayya!”

28. Nan da nan sai ya shahara a ko'ina duk kewayen ƙasar Galili.

29. Da fitarsu daga majami'a, sai suka shiga gidan su Bitrus da Andarawas, tare da Yakubu da Yahaya.

Karanta cikakken babi Mar 1