2. ya kuma aike su su yi wa'azin Mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3. Ya kuma ce musu, “Kada ku ɗauki wani guzuri a tafiyarku, ko sanda, ko burgami, ko gurasa, ko kuɗi. Kada kuma ku ɗauki taguwa biyu.
4. Duk gidan da kuka sauka, ku zauna a nan har ku tashi.
5. Duk waɗanda ba su yi na'am da ku ba, in za ku bar garin, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”