Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 7:11-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Ba da daɗewa ba, Yesu ya tafi wani gari, wai shi Nayin, almajiransa da kuma babban taro suka tafi da shi.

12. Ya kusaci ƙofar garin ke nan, sai ga wani mamaci ana ɗauke da shi, shi kaɗai ne wajen uwa tasa, mijinta kuwa ya mutu. Mutanen gari da yawa sun rako ta.

13. Da Ubangiji ya gan ta, ya ji tausayinta, ya kuma ce mata, “Daina kuka.”

14. Sa'an nan ya matso, ya taɓa makarar, masu ɗauka kuma suka tsaya cik. Sai Yesu ya ce, “Samari, na ce maka ka tashi.”

15. Mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuwa ya ba da shi ga uwa tasa.

16. Sai tsoro ya kama su duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Lalle, wani annabi mai girma ya bayyana a cikinmu,” da kuma, “Allah ya kula da jama'arsa.”

17. Wannan labarin nasa kuwa ya bazu a dukan ƙasar Yahudiya da kewayenta.

Karanta cikakken babi Luk 7