Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 6:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Sai ya duddube su duke, ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Ya miƙa, hannunsa kuwa sai ya koma lafiyayye.

11. Sai suka husata ƙwarai, suka yi shawarar abin da za su yi wa Yesu.

12. A kwanakin nan Yesu ya fita ya hau dutse domin yin addu'a. Dare farai yana addu'a ga Allah.

13. Da gari ya waye ya kira almajiransa, ya zaɓi goma sha biyu a cikinsu, ya ce da su manzanni.

14. Su ne Bitrus, da ɗan'uwansa Andarawas, da Yakubu, da Yahaya, da Filibus, da Bartalamawas,

Karanta cikakken babi Luk 6