29. Sai suka tashi suka fitar da shi bayan gari, har suka kai shi goshin dutsen da aka gina garinsu a kai, don su jefa shi ƙasa.
30. Amma ya ratsa ta tsakiyarsu, ya yi tafiyarsa.
31. Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a ƙasar Galili, yana koya musu ran Asabar.
32. Suka yi mamakin koyarwarsa domin magana tasa da hakikancewa take.
33. A majami'ar kuwa akwai wani mutum mai baƙin aljan. Sai ya ta da murya da ƙarfi ya ce,