Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 4:20-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Ya rufe littafin ya mayar wa mai hidima, ya zauna. Duk waɗanda suke cikin majami'a suka zuba masa ido.

21. Sai ya fara ce musu, “Yau Nassin nan ya cika a kunnenku.”

22. Duk suka yabe shi, suna mamakin maganarsa ta alheri da ya faɗa, har suka ce, “Ashe, wannan ba ɗan Yusufu ba ne?”

23. Yesu ya ce musu, “Lalle za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka.’ Za ku kuma ce mini, ‘Duk abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, ka yi a nan garinku mana.’ ”

24. Ya ce kuma, “Hakika, ina gaya muku, ba annabin da yake yardajje a garinsu.

25. Amma gaskiya nake gaya muku, a zamanin Iliya akwai mata gwauraye da yawa a Isra'ila, wato a lokacin da aka hana ruwan sama har shekara uku da wata shida, sa'ad da babbar yunwa ta game dukan ƙasar.

Karanta cikakken babi Luk 4