Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 24:43-53 Littafi Mai Tsarki (HAU)

43. Ya kuwa karɓa, ya ci a gabansu.

44. Ya kuma ce musu, “Wannan ita ce maganata da na gaya muku tun muna tare, cewa lalle ne a cika duk abin da yake rubuce game da ni a Attaura ta Musa, da littattafan annabawa, da kuma Zabura.”

45. Sa'an nan ya wayar da hankalinsu su fahimci Littattafai,

46. ya kuma ce musu, “Haka yake a rubuce, cewa wajibi ne Almasihu ya sha wuya, a rana ta uku kuma ya tashi daga matattu,

47. a kuma yi wa dukan al'ummai wa'azi su tuba, a gafarta musu zunubansu saboda sunansa. Za a kuwa fara daga Urushalima.

48. Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.

49. Ga shi, ni zan aiko muku da abin da Ubana ya alkawarta. Amma ku dakata a birni tukuna, har a yi muku baiwar iko daga Sama.”

50. Sai ya kai su waje har jikin Betanya. Ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.

51. Yana sa musu albarka ke nan, sai ya rabu da su, aka ɗauke shi zuwa sama.

52. Su kuwa suka yi masa sujada, suka koma Urushalima, suna matuƙar farin ciki.

53. Ko yaushe kuma suna a Haikali suna yabon Allah.

Karanta cikakken babi Luk 24