40. Da ya faɗi haka, ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41. Amma tun suna da sauran shakka saboda tsananin farin ciki da mamaki, sai ya ce musu, “Kuna da wani abinci a nan?”
42. Sai suka ba shi wata tsokar gasasshen kifi.
43. Ya kuwa karɓa, ya ci a gabansu.
44. Ya kuma ce musu, “Wannan ita ce maganata da na gaya muku tun muna tare, cewa lalle ne a cika duk abin da yake rubuce game da ni a Attaura ta Musa, da littattafan annabawa, da kuma Zabura.”
45. Sa'an nan ya wayar da hankalinsu su fahimci Littattafai,
46. ya kuma ce musu, “Haka yake a rubuce, cewa wajibi ne Almasihu ya sha wuya, a rana ta uku kuma ya tashi daga matattu,
47. a kuma yi wa dukan al'ummai wa'azi su tuba, a gafarta musu zunubansu saboda sunansa. Za a kuwa fara daga Urushalima.