Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 24:37-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

37. Amma suka firgita, tsoro ya kama su, suka zaci fatalwa suke gani.

38. Sai ya ce musu, “Don me kuka firgita, kuke kuma tantama a zuciyarku?

39. Ku dubi hannuwana da ƙafafuna, ai, ni ne da kaina. Ku taɓa ni, ku ji, don fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”

40. Da ya faɗi haka, ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.

41. Amma tun suna da sauran shakka saboda tsananin farin ciki da mamaki, sai ya ce musu, “Kuna da wani abinci a nan?”

42. Sai suka ba shi wata tsokar gasasshen kifi.

43. Ya kuwa karɓa, ya ci a gabansu.

Karanta cikakken babi Luk 24