Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 24:34-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. suna cewa, “Hakika Ubangiji ya tashi, har ya bayyana ga Bitrus!”

35. Su kuma suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane shi a wajen gutsura gurasa.

36. Suna cikin faɗar waɗannan abubuwa, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu, ya ce musu, “Salama alaikun!”

37. Amma suka firgita, tsoro ya kama su, suka zaci fatalwa suke gani.

38. Sai ya ce musu, “Don me kuka firgita, kuke kuma tantama a zuciyarku?

39. Ku dubi hannuwana da ƙafafuna, ai, ni ne da kaina. Ku taɓa ni, ku ji, don fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”

40. Da ya faɗi haka, ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.

41. Amma tun suna da sauran shakka saboda tsananin farin ciki da mamaki, sai ya ce musu, “Kuna da wani abinci a nan?”

42. Sai suka ba shi wata tsokar gasasshen kifi.

43. Ya kuwa karɓa, ya ci a gabansu.

44. Ya kuma ce musu, “Wannan ita ce maganata da na gaya muku tun muna tare, cewa lalle ne a cika duk abin da yake rubuce game da ni a Attaura ta Musa, da littattafan annabawa, da kuma Zabura.”

45. Sa'an nan ya wayar da hankalinsu su fahimci Littattafai,

Karanta cikakken babi Luk 24