Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 24:3-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji ba.

4. Tun suna cikin damuwa da abin, sai kawai ga waɗansu mutum biyu a tsaye kusa da su, saye da tufafi masu ƙyalƙyali.

5. Don tsoro, matan suka sunkuyar da kansu ƙasa. Mutanen suka ce musu, “Don me kuke neman rayayye a cikin matattu?

6. Ai, ba ya nan, ya tashi. Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana Galili

7. cewa, ‘Lalle ne a ba da Ɗan Mutum ga mutane masu zunubi, a gicciye shi, a rana ta uku kuma ya tashi’.”

Karanta cikakken babi Luk 24