3. Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji ba.
4. Tun suna cikin damuwa da abin, sai kawai ga waɗansu mutum biyu a tsaye kusa da su, saye da tufafi masu ƙyalƙyali.
5. Don tsoro, matan suka sunkuyar da kansu ƙasa. Mutanen suka ce musu, “Don me kuke neman rayayye a cikin matattu?
6. Ai, ba ya nan, ya tashi. Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana Galili
7. cewa, ‘Lalle ne a ba da Ɗan Mutum ga mutane masu zunubi, a gicciye shi, a rana ta uku kuma ya tashi’.”