Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 20:39-47 Littafi Mai Tsarki (HAU)

39. Sai waɗansu malaman Attaura suka amsa suka ce, “Malam, ka faɗi daidai.”

40. Daga nan kuma ba su yi ƙarfin halin tambayarsa wani abu ba.

41. Amma ya ce musu, “Ƙaƙa za su ce Almasihu ɗan Dawuda ne?

42. Domin Dawuda da kansa a Zabura ya ce,‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,“Zauna a damana,

43. Sai na sa ka take maƙiyanka.” ’

44. Dawuda ya ce shi Ubangiji ne. To, ƙaƙa zai zama ɗansa?”

45. Ya ce wa almajiransa a gaban dukan jama'a,

46. “Ku yi hankali da malaman Attaura, masu son yawo a cikin manyan riguna, masu so a gaishe su a kasuwa, masu son mafifitan mazaunai a majami'u, da mazaunan alfarma a wurin biki.

47. Su ne masu cin kayan matan da mazansu suka mutu, masu yin doguwar addu'a don ɓad da sawu. Su za a yi wa hukunci mafi tsanani.”

Karanta cikakken babi Luk 20