Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 2:28-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. sai Saminu ya rungume shi, ya yi wa Allah godiya, ya ce,

29. “Yanzu kam, ya Mamallaki,Sai ka sallami bawanka lafiya,Bisa ga abin da ka faɗa,

30. Don na ga cetonka zahiri,

31. Da ka shirya a gaban kabilai duka,

32. Haske mai bayyana wa alummai hanyarka,Da kuma ɗaukakar jama'arka Isra'ila.”

33. Uwa tasa da ubansa kuwa suna mamakin abin da aka faɗa game da shi,

34. Sai Saminu ya sa musu albarka, ya ce wa Maryamu uwar Yesu,“Kin ga wannan yaro, shi aka sa ya zama sanadin faɗuwar waɗansu, tashin waɗansu kuma da yawa cikin Isra'ila,Zai kuma zama alama wadda ake kushenta,

35. Domin tunanin zukata da yawa su bayyana.I, ke ma, takobi zai tsaga zuciyarki.”

36. Akwai kuma wata annabiya, mai suna Hannatu, 'yar Fanuyila, na kabilar Ashiru. Ta kuwa tsufa ƙwarai, ta yi zaman aure shekara bakwai bayan ɗaukanta na budurci,

37. da mijinta ya mutu kuma ta yi zaman gwauranci har shekara tamanin da huɗu. Ba ta rabuwa da Haikalin, tana bauta wa Allah dare da rana ta wurin yin addu'a da azumi.

Karanta cikakken babi Luk 2