Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:7-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Amma ba su da ɗa, don Alisabatu bakararriya ce, dukansu biyu kuma sun tsufa.

8. Ana nan, wata rana Zakariya na kan hidima tasa ta firist, a sa'ad da hidimar ta kewayo kan ƙungiyarsu,

9. bisa ga al'adar hidimar firistoci, sai kuri'a ta nuna shi ne mai shiga Haikalin Ubangiji, ya ƙona turare.

10. A lokacin ƙona turare kuwa duk taron jama'a suna waje, suna addu'a,

11. sai wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, yana tsaye a dama da bagadin ƙona turare.

12. Da Zakariya ya gan shi ya firgita, tsoro ya kama shi.

13. Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro Zakariya, an karɓi addu'arka, matarka Alisabatu za ta haifa maka ɗa, za ka kuma sa masa suna Yahaya.

14. Za ka yi murna da farin ciki,Mutane da yawa kuma za su yi farin ciki da haihuwa tasa.

15. Domin zai zama mai girma a wurin Ubangiji,Ba kuwa zai sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba.Za a cika shi da Ruhu Mai TsarkiTun yana cikin uwa tasa.

16. Zai kuma juyo da Isra'ilawa da yawa ga Ubangiji Allahnsu.

Karanta cikakken babi Luk 1