Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:63-68 Littafi Mai Tsarki (HAU)

63. Sai ya nema a ba shi allo, sa'an nan ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Duka suka yi mamaki.

64. Nan da nan ya sami baki, kwaɗon harshensa ya saku, ya fara magana, yana yabon Allah.

65. Sai tsoro ya kama dukan maƙwabtansu. Aka yi ta baza labarin duk waɗannan al'amura ko'ina a dukan ƙasa mai duwatsu ta Yahudiya.

66. Duk waɗanda suka ji kuwa suka riƙe a zuciyarsu, suna cewa, “Me ke nan ɗan yaron nan zai zama?” Gama ikon Ubangiji yana tare da shi.

67. Sai aka cika ubansa Zakariya da Ruhu Mai Tsarki, ya yi annabci, ya ce,

68. “Ubangiji Allahn Isra'ila,A gare shi ne lalle yabo yake tabbata,Domin ya kula, ya yi wa jama'a tasa fansa.

Karanta cikakken babi Luk 1