Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:60-66 Littafi Mai Tsarki (HAU)

60. amma uwa tasa ta ce, “A'a, Yahaya za a sa masa.”

61. Sai suka ce mata, “Ai kuwa, ba wani ɗan'uwanku mai suna haka.”

62. Sai suka alamta wa ubansa, suna neman sunan da yake so a sa masa.

63. Sai ya nema a ba shi allo, sa'an nan ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Duka suka yi mamaki.

64. Nan da nan ya sami baki, kwaɗon harshensa ya saku, ya fara magana, yana yabon Allah.

65. Sai tsoro ya kama dukan maƙwabtansu. Aka yi ta baza labarin duk waɗannan al'amura ko'ina a dukan ƙasa mai duwatsu ta Yahudiya.

66. Duk waɗanda suka ji kuwa suka riƙe a zuciyarsu, suna cewa, “Me ke nan ɗan yaron nan zai zama?” Gama ikon Ubangiji yana tare da shi.

Karanta cikakken babi Luk 1