Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:38-47 Littafi Mai Tsarki (HAU)

38. Sai Maryamu ta ce, “To, ga shi, ni baiwar Ubangiji ce, yă zama mini yadda ka faɗa.” Sai mala'ikan ya tashi daga gare ta.

39. A kwanakin nan Maryamu ta tashi da hanzari, ta tafi wata ƙasa mai duwatsu, zuwa wani gari na ƙasar Yahuza.

40. Ta shiga gidan Zakariya ta gai da Alisabatu.

41. Sai ya zamana da Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, jariri ya motsa da ƙarfi a cikinta. Aka kuwa cika Alisabatu da Ruhu Mai Tsarki,

42. har ta tā da murya da ƙarfi, ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata, ɗan cikinki kuma mai albarka ne!

43. Ta yaya wannan alheri ya same ni, har da uwar Ubangijina za ta zo gare ni?

44. Domin kuwa da jin muryarki ta gaisuwa a kunnena, sai jaririn ya motsa da ƙarfi a cikina domin farin ciki.

45. Albarka tā tabbata ga wadda ta gaskata, domin za a cika abubuwan da Ubangiji ya aiko a faɗa mata.”

46. Sai Maryamu ta ce,“Zuciyata na ɗaukaka shi, Ubangiji,

47. Allah Mai Cetona, da shi ruhuna yake ta farin ciki,

Karanta cikakken babi Luk 1