Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:33-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

33. Zai kuma mallaki zuriyar Yakubu har abada,Mulkinsa kuwa ba shi da matuƙa.”

34. Sai Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Ƙaƙa wannan zai yiwu, tun da yake ba a kai ni ɗaki ba?”

35. Mala'ikan ya amsa mata ya ce,“Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki,Ikon Maɗaukaki kuma zai lulluɓe ki.Saboda haka Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.

36. Ga shi kuma, 'yar'uwarki Alisabatu ma ta yi cikin ɗa namiji da tsufanta, wannan kuwa shi ne watanta na shaida, ita da ake ce wa bakararriya.

37. Ba wata faɗar Allah da za ta kasa cika.”

Karanta cikakken babi Luk 1