Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:32-42 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki.Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dawuda,

33. Zai kuma mallaki zuriyar Yakubu har abada,Mulkinsa kuwa ba shi da matuƙa.”

34. Sai Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Ƙaƙa wannan zai yiwu, tun da yake ba a kai ni ɗaki ba?”

35. Mala'ikan ya amsa mata ya ce,“Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki,Ikon Maɗaukaki kuma zai lulluɓe ki.Saboda haka Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.

36. Ga shi kuma, 'yar'uwarki Alisabatu ma ta yi cikin ɗa namiji da tsufanta, wannan kuwa shi ne watanta na shaida, ita da ake ce wa bakararriya.

37. Ba wata faɗar Allah da za ta kasa cika.”

38. Sai Maryamu ta ce, “To, ga shi, ni baiwar Ubangiji ce, yă zama mini yadda ka faɗa.” Sai mala'ikan ya tashi daga gare ta.

39. A kwanakin nan Maryamu ta tashi da hanzari, ta tafi wata ƙasa mai duwatsu, zuwa wani gari na ƙasar Yahuza.

40. Ta shiga gidan Zakariya ta gai da Alisabatu.

41. Sai ya zamana da Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, jariri ya motsa da ƙarfi a cikinta. Aka kuwa cika Alisabatu da Ruhu Mai Tsarki,

42. har ta tā da murya da ƙarfi, ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata, ɗan cikinki kuma mai albarka ne!

Karanta cikakken babi Luk 1