Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Gal 1:18-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Bayan shekara uku kuma sai na tafi Urushalima ganin Kefas, na kuwa kwana goma sha biyar a gunsa.

19. Amma ban ga ko ɗaya a cikin sauran manzanni ba, sai dai Yakubu ɗan'uwan Ubangiji.

20. Abin nan da nake rubuto muku fa, ba ƙarya nake yi ba, a gaban Allah nake faɗa.

21. Daga baya kuma, na tafi ƙasar Suriya da ta Kilikiya.

22. Amma kuwa ikilisiyoyin Almasihu da suke a ƙasar Yahudiya, ba su san ni ido da ido ba tukuna.

23. Sai dai kawai sun ji an ce, “Wanda dā yake tsananta mana, ga shi, a yanzu yana sanar da bangaskiyar nan da dā yake ta rusawa!”

24. Sai suka ɗaukaka Allah saboda ni.

Karanta cikakken babi Gal 1