Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fil 1:18-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Ko ma ya yi maka wani laifi, ko kuwa kana binsa wani abu, sai ka mai da shi a kaina.

19. Ni Bulus, ni nake rubuto wannan da hannuna, ni kuwa zan biya, kada ma a yi zancen ranka da na fanso maka!

20. Ya ɗan'uwana, ka yarda in sami wata fa'ida a gare ka saboda Ubangiji! Ka sanyaya mini zuciya saboda Almasihu.

21. Don na tabbatar da biyayyarka, shi ya sa na rubuto maka, don na sani za ka yi, har fiye da abin da na faɗa.

22. Har wa yau kuma, ka shirya mini masauki, domin ina sa zuciya a ba ni yarjin zuwa gare ku albarkacin addu'arku.

23. Abafaras, abokin ɗaurina saboda Almasihu Yesu, yana gaishe ka,

24. haka kuma Markus, da Aristarkus, da Dimas, da Luka, abokan aikina, suna gaishe ka.

25. Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a zukatanku.

Karanta cikakken babi Fil 1