Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fil 1:17-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Saboda haka in ka ɗauke ni a kan abokin tarayya, to, sai ka karɓe shi kamar yadda za ka karɓe ni.

18. Ko ma ya yi maka wani laifi, ko kuwa kana binsa wani abu, sai ka mai da shi a kaina.

19. Ni Bulus, ni nake rubuto wannan da hannuna, ni kuwa zan biya, kada ma a yi zancen ranka da na fanso maka!

20. Ya ɗan'uwana, ka yarda in sami wata fa'ida a gare ka saboda Ubangiji! Ka sanyaya mini zuciya saboda Almasihu.

Karanta cikakken babi Fil 1