Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:42-51 Littafi Mai Tsarki (HAU)

42. Saboda haka Allah ya juya musu baya, ya sallame su ga bautar taurari, yadda yake a rubuce a littafin annabawa cewa,‘Ya ku jama'ar Isra'ila,Ni ne kuka yanka wa dabbobi, kuka miƙa wa hadaya,Har shekara arba'in a cikin jeji?

43. Ai, yawo kuka yi da alfarwar Molek,Da surar tauraron gunki Ramfan,Wato surorin nan da kuka ƙera don ku yi musu sujada.Ni kuwa zan kawar da ku a can bayan Babila.’

44. “Dā kakanninmu suna da alfarwar shaida a jeji, irin wadda mai maganar nan da Musa ya umarta a yi, daidai fasalin da ya gani.

45. Alfarwan nan ita ce kakanninmu suka gāda, suka kuma kawo ƙasar nan a zamanin Joshuwa, bayan sun mallake ƙasar al'umman da Allah ya kora a gaban idonsu. Alfarwan nan kuwa tana nan har ya zuwa zamanin Dawuda,

46. wanda ya sami tagomashi wurin Allah, har ya nemi alfarmar yi wa Allahn Yakubu masujada.

47. Amma Sulemanu ne ya yi wa Allah gini.

48. Duk da haka Maɗaukaki ba ya zama a gidaje, ginin mutum. Yadda Annabi Ishaya ya ce,

49. ‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina,Ƙasa kuwa matashin ƙafata.Wane wuri kuma za ku gina mini?Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna?

50. Ba da ikona na halicci dukan waɗannan abubuwa ba?’

51. “Ku kangararru, masu ɓatan basira, masu kunnen ƙashi, kullum kuna yi wa Ruhu Mai Tsarki tsayayya. Yadda kakanninku suka yi, haka ku ma kuke yi.

Karanta cikakken babi A.m. 7