Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 3:18-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Amma ta haka Allah ya cika faɗar da ya riga ya yi ta bakin annabawa duka, cewa Almasihunsa zai sha wuya.

19. Saboda haka sai ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, Ubangiji kuma kansa ya riƙa wartsakar da ku,

20. ya kuma aiko da Almasihun da aka ƙaddara muku tun dā, wato Yesu,

21. wanda lalle ne ya zauna a Sama, har kafin lokacin nan na sabunta dukkan abubuwa da Allah ya faɗa tun zamanin dā ta bakin annabawansa tsarkaka.

22. Musa ma ya ce, ‘Ubangiji Allah zai tasar muku da wani annabi daga cikin 'yan'uwanku, kamar yadda ya tashe ni. Lalle ne ku saurari duk abin da ya faɗa muku.

23. Zai zamana kuma duk wanda ya ƙi sauraron annabin nan, za a hallaka shi daga cikin jama'a.’

Karanta cikakken babi A.m. 3