Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 26:6-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ai, saboda na sa zuciya ga cikar alkawarin nan ne da Allah ya yi wa kakanninmu nake nan a tsaye a yi mini shari'a.

7. Alkwarin nan kuwa, shi ne wanda kabilanmu goma sha biyu suke himmantuwa ga bauta wa Allah dare da rana, suna sa zuciya su ga cikarsa. Saboda sa zuciyar nan kuma fa Yahudawa suke ƙarata, ya sarki!

8. Yaya cewa Allah yana ta da matattu sa'an nan, ya ƙi gaskatuwa a gare ku?

9. “To, ni kaina ma a dā na ga kamar wajibi ne in yi abubuwa da yawa, na gāba da sunan Yesu Banazare.

10. Na kuwa yi haka a Urushalima, har na sami izini daga manyan firstoci, na kulle tsarkaka da yawa a kurkuku. Har ma a lokacin da ake kashe su ina goyon bayan yin haka.

11. Na kuma sha gwada musu azaba a dukan majami'u, ina ƙoƙarin sa su yin saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.”

12. “Cikin halin haka ne, ina tafiya Dimashƙu da izinin manyan firistoci da kuma saƙonsu,

Karanta cikakken babi A.m. 26