Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 2:17-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. ‘Allah ya ce,A zamanin karshe zai zamanto zan zubo wa dukan 'yan adam Ruhuna.'Ya'yanku mata da maza za su yi annabci,Wahayi zai zo wa samarinku,Dattawanku kuma za su yi mafarkai.

18. Hakika, har ma a kwanakin nan zan zubo Ruhuna a kan bayina mata da maza,Za su kuma yi annabci.

19. Zan nuna abubuwan al'ajabi a sararin sama,Da mu'ujizai a nan ƙasa,Wato jini, da wuta, da kuma, hauhawan hayaƙi.

20. Za a mai da rana duhu,Wata kuma jini,Kafin Ranar Ubangiji ta zo,Babbar ranar nan mai girma.

21. A sa'an nan ne zai zamanto kowa ya yi addu'a da sunan Ubangiji zai sami ceto.’

22. “Ya ku 'yan'uwa, Isra'ilawa, ku ji wannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar muku cewa shi yardajjensa ne, ta mu'ujizai, da abubuwan al'ajabi, da alamu waɗanda ya yi ta wurinsa a cikinku, kamar yadda ku kanku kuka sani,

23. shi Yesun nan fa, an ba da shi bisa ƙaddarar Allah da rigyasaninsa, ku kuwa kuka gicciye shi, kuka kashe shi, ta hannun masu zunubi.

24. Amma Allah ya tashe shi bayan ya ɓalle masa ƙangin mutuwa, domin ba shi yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.

25. Dawuda kuma ya yi faɗi a game da shi ya ce,‘Kullum hankalina yana kan Ubangiji,Yana damana, domin kada in jijjigu.

26. Saboda haka, zuciyata ta yi fari, ina farin ciki matuƙa.Ko da yake kuma ni jiki ne, zan zauna ina sa zuciya,

27. Domin ba za ka yar da raina a Hades ba,Ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.

28. Kā sanar da ni hanyoyin rai.Za ka cika ni da farin ciki ta zamana a zatinka.’

29. Ya 'yan'uwa, na iya yi muku magana da amincewa a game da kakanmu Dawuda, cewa ya mutu, an binne shi, kabarinsa kuma yana nan gare mu har ya zuwa yau.

30. To, da yake shi annabi ne, ya kuma san Allah ya rantse masa, cewa zai ɗora wani daga cikin zuriya tasa kan kursiyinsa,

31. sai ya hango, ya kuma yi faɗi a kan tashin Almasihu daga matattu, cewa ba za a yashe shi a Hades ba, jikinsa kuwa ba zai ruɓa ba.

32. Yesun nan kam, Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa duk shaidu ne ga haka.

33. Da yake an ɗaukaka shi a dama ga Allah, ya kuma sami cikar alkawarin nan na baiwar Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, sai ya zubo da wannan da kuke gani, kuke kuma ji.

Karanta cikakken babi A.m. 2