Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 19:3-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Sai ya ce, “To, wace baftisma ke nan aka yi muku?” Suka ce, “Irin ta Yahaya ce.”

4. Bulus ya ce, “Ai, Yahaya baftisma ya yi a tuba, yana faɗa wa mutane su gaskata da mai zuwa bayansa, wato Yesu.”

5. Da suka ji haka, aka yi musu baftisma da sunan Ubangiji Yesu.

6. Da Bulus ya ɗora musu hannu, Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu, suka kuwa yi magana da waɗansu harsuna, suna annabci.

Karanta cikakken babi A.m. 19