Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 15:19-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa al'ummai waɗanda suke juyowa ga Allah,

20. sai dai mu rubuta musu wasiƙa, su guji abubuwan ƙazanta na game da gumaka, da fasikanci, da cin abin da aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini.

21. Domin tun zamanin dā, a kowane gari akwai masu yin wa'azi da littattafan Musa, ana kuma karanta su a majami'u kowace Asabar.”

22. Sai manzanni da dattawan Ikkilisiya, tare da dukan 'yan Ikkilisiya, suka ga ya kyautu su zaɓi waɗansu daga cikinsu, su aike su Antakiya tare da Bulus da Barnaba. Sai suka aiki Yahuza, wanda ake kira Barsaba, da kuma Sila, shugabanni ne cikin 'yan'uwa,

Karanta cikakken babi A.m. 15