Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 15:12-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Sai duk taron mutane suka yi tsit, suka saurari Barnaba da Bulus, sa'ad da suke ba da labarin mu'ujizai da abubuwan al'ajabi, da Allah ya yi ga al'ummai ta wurinsu.

13. Bayan sun gama jawabi, Yakubu ya amsa ya ce, “Ya ku 'yan'uwa, ku saurare ni.

14. Bitrus ya ba da labari yadda Allah ya fara kula da al'ummai, domin ya keɓe wata jama'a daga cikinsu ta zama tasa.

15. Wannan kuwa daidai yake da maganar annabawa, yadda yake a rubuce cewa,

16. ‘Bayan haka kuma zan komo,In sāke gina gidan Dawuda da ya rushe,In sāke ta da kangonsa,In tsai da shi,

17. Domin sauran mutane su nemi Ubangiji,Wato al'umman da suke nawa.’

18. Haka Ubangiji ya ce, shi da ya bayyana waɗannan abubuwa tun zamanin dā.

19. Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa al'ummai waɗanda suke juyowa ga Allah,

20. sai dai mu rubuta musu wasiƙa, su guji abubuwan ƙazanta na game da gumaka, da fasikanci, da cin abin da aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini.

21. Domin tun zamanin dā, a kowane gari akwai masu yin wa'azi da littattafan Musa, ana kuma karanta su a majami'u kowace Asabar.”

22. Sai manzanni da dattawan Ikkilisiya, tare da dukan 'yan Ikkilisiya, suka ga ya kyautu su zaɓi waɗansu daga cikinsu, su aike su Antakiya tare da Bulus da Barnaba. Sai suka aiki Yahuza, wanda ake kira Barsaba, da kuma Sila, shugabanni ne cikin 'yan'uwa,

23. da wannan takarda cewa, “Daga 'yan'uwanku, manzanni da dattawan Ikkilisiya, zuwa ga 'yan'uwanmu na al'ummai a Antakiya da ƙasar Suriya da ta Kilikiya. Gaisuwa mai yawa.

24. Tun da muka sami labari, cewa waɗansu daga cikinmu sun ta da hankalinku da maganganu, suna ruɗa ku, ko da yake ba mu umarce su da haka ba,

25. sai muka ga ya kyautu, da yake bakinmu ya zo ɗaya, mu aiko muku waɗansu zaɓaɓɓun mutane, tare da ƙaunatattunmu Barnaba da Bulus,

26. waɗanda suka sayar da ransu saboda sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu.

27. Don haka, ga shi, mun aiko muku Yahuza da Sila, su ma za su gaya muku waɗannan abubuwa da bakinsu.

Karanta cikakken babi A.m. 15