Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 11:2-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Da Bitrus ya zo Urushalima, 'yan ɗariƙar masu kaciyar nan suka yi masa sūka,

3. suka ce, “Ga shi, ka shiga wurin marasa kaciya, har ka ci abinci tare da su!”

4. Sai Bitrus ya fara, yana yi musu bayani bi da bi cewa,

5. “Ni dai, ina birnin Yafa ina addu'a, sai wahayi ya zo mini, na ga wani abu na saukowa kamar babban mayafi, an zuro shi daga sama ta kusurwoyinsa huɗu, har ya zo wurina.

6. Da na zuba masa ido, na duba na ga dabbobi, da namomin jeji, da masu jan ciki, da kuma tsuntsaye a ciki.

7. Sai kuma na ji wata murya ta ce mini, ‘Bitrus, ka tashi, ka yanka, ka ci.’

8. Amma na ce, ‘A'a, ya Ubangiji, don ba wani abu marar tsarki ko mai ƙazanta da ya taɓa shiga bakina.’

9. Sai muryar ta amsa daga Sama ta yi magana ta biyu, ta ce, ‘Abin da Allah ya tsarkake, kada ka ce da shi marar tsarki.’

Karanta cikakken babi A.m. 11