Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 10:18-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. suna sallama, suna tambaya ko Saminu da ake kira Bitrus a nan ya sauka.

19. Tun Bitrus yana bibiya wahayin nan, Ruhu ya ce masa, “Ga mutum uku nan suna nemanka.

20. Tashi, ka sauka, ku tafi tare, ba da wata shakka ba, domin ni ne na aiko su.”

21. Sai Bitrus ya sauka wurin mutanen, ya ce musu, “Ga ni, ni ne kuke nema. Wace magana yake tafe da ku?”

22. Sai suka ce, “Wani jarumi ne, wai shi Karniliyas, mutumin kirki, mai tsoron Allah, wanda duk jama'ar Yahudawa suke yabo, shi ne wani tsattsarkan mala'ika ya umarce shi, ya aiko ka je gidansa, ya ji maganarka.”

23. Sai Bitrus ya shigo da su, ya sauke su.Kashegari ya tashi suka tafi tare, waɗansu 'yan'uwa kuma daga Yafa suka raka shi.

24. Kashegari kuma suka shiga Kaisariya. Dā ma Karniliyas na tsammaninsu, har ya gayyato 'yan'uwansa da aminansa.

25. Bitrus na shiga gidan ke nan sai Karniliyas ya tarye shi, ya fāɗi a gabansa, ya yi masa sujada.

Karanta cikakken babi A.m. 10