Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Afi 5:6-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Kada wani ya hilace ku da maganar wofi, gama sabili da waɗannan zunubai ne fushin Allah yake aukawa a kan kangararru.

7. Saboda haka, kada ku yi cuɗanya da su,

8. domin dā ku duhu ne, amma a yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi zaman mutanen haske,

9. domin haske shi ne yake haifar duk abin da yake nagari, na adalci, da na gaskiya.

10. Ku dai tabbata abin zai gamshi Ubangiji.

11. Ku yi nesa da ayyukan duhu na banza da wofi, sai dai ku tona su.

Karanta cikakken babi Afi 5