Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Afi 5:5-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Kun dai tabbata, ba wani fasiki, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayi (wanda shi da mai bautar gumaka duk ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Almasihu da na Allah.

6. Kada wani ya hilace ku da maganar wofi, gama sabili da waɗannan zunubai ne fushin Allah yake aukawa a kan kangararru.

7. Saboda haka, kada ku yi cuɗanya da su,

8. domin dā ku duhu ne, amma a yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi zaman mutanen haske,

9. domin haske shi ne yake haifar duk abin da yake nagari, na adalci, da na gaskiya.

10. Ku dai tabbata abin zai gamshi Ubangiji.

Karanta cikakken babi Afi 5