Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tim 2:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Da farko dai ina gargaɗi, cewa a yi ta roƙon Allah, ana addu'a, ana godo, ana gode wa Allah saboda dukkan mutane,

2. da sarakuna da kuma duk waɗanda suke a manyan maƙamai, don mu zauna lafiya, rai a kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.

3. Wannan kyakkyawan abu ne, kuma abin karɓa ne a gun Allah Mai Cetonmu,

4. wanda yake son dukkan mutane su sami ceto, su kuma kai ga sanin gaskiya.

5. Domin Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya ne, a tsakanin Allah da mutane, Almasihu Yesu, mutum,

6. wanda ya ba da kansa fansa saboda kowa da kowa. An kuwa yi shaidar wannan a daidai lokacinsa.

7. Don haka ne aka sa ni mai wa'azi, da manzo kuma (gasikya nake faɗa, ba ƙarya ba), mai koya wa al'ummai al'amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.

Karanta cikakken babi 1 Tim 2