Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tas 5:15-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Ku lura fa, kada kowa ya rama mugunta da mugunta. Sai dai kullum ku nace yi wa juna aiki nagari, da kuma dukkan mutane.

16. Ku riƙa yin farin ciki a kullum.

17. Ku riƙa yin addu'a ba fāsawa.

18. Ku godiya ga Allah a kowane hali, domin shi ne nufin Allah a game da ku ta wurin Almasihu Yesu.

19. Kada ku danne maganar Ruhu.

20. Kada ku raina annabci,

21. sai dai ku jarraba kome, ku riƙi abin da yake nagari kankan.

22. Ku yi nesa da kowace irin mugunta.

23. Allah kansa, mai zartar da salama, yă tsarkake ku sarai, ya kuma kiyaye ruhunku da ranku da jikinku ƙalau, ku kasance marasa abin zargi a ranar komowar Ubangijinmu Yesu Almasihu.

24. Wanda yake kiranku ɗin nan mai alkawari ne, zai kuwa zartar.

25. Ya ku 'yan'uwa, ku yi mana addu'a.

26. Ku gai da dukkan 'yan'uwa da tsattsarkar sumba.

Karanta cikakken babi 1 Tas 5