Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 7:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. To, a yanzu, a game da abin da kuka rubuto, yana da kyau mutum ya zauna ba aure.

2. Amma don gudun fasikanci sai kowane mutum ya kasance da matarsa, kowace mace kuma da mijinta.

3. Miji yă ba matarsa hakkinta na aure, haka kuma matar ga mijinta.

4. Matar kuwa ba ta da iko da jikinta, sai dai mijin, haka kuma mijin ba shi da iko da jikinsa, sai dai matar.

5. Kada ɗayanku yă ƙaurace wa ɗaya, sai ko da yardar juna zuwa wani ɗan lokaci kaza, don ku himmantu ga addu'a, sa'an nan ku sāke haɗuwa, kada Shaiɗan yă zuga ku ta wajen rashin kamewa.

Karanta cikakken babi 1 Kor 7